GAYYATA TA MUSAMMAN DOMIN GABATAR DA CAK NA SAYAWA GWAMNA BELLO MATAWALLE FOM DIN TAKARAR GWAMNAN ZAMFARA A 2023

Sakamakon nuna yarda da gamsuwa da jagorancin Hon. Dr. Bello Muhammad Matawallen Maradun, Kimanin kungiyoyin jihar Zamfara 102 suka yi karo-karo suka tara naira miliyan 50 domin saya masa fom din takarar gwamna Karo na biyu a 2023



Saboda haka ne jam'iyar Apc ta jihar Zamfara ke gayyatar dukkanin halatattun yayan jam'iyar Apc na jihar zuwa wajen gangamin gabatar da cak din ga mai daraja Gwamnan jihar Zamfara Hon Dr. Bello Muhammad Matawallen Maradun karkashin jagorancin Shugaban jam'iyar Apc na jihar Zamfara Hon. Tukur Umar Danfulani 

Za a hadu a Babban Masallacin idi da ke Tudun Wada Gusau da karfe 8:00 na safe ranar Jumu'a 6/5/2022 inda za a taka zuwa Fadar gwamnatin jihar domin mika cak din ga Gwamnan 

Shugaban jam'iyar na kara nuna godiyarsa ga Allah da al'ummar jihar Zamfara akan irin Soyayya da su ke nunawa gwamnatinsu tare da rokonsu da su cigaba da baiwa gwamnatin goyon baya.

Haka zalika Shugaban ya nuna matukar godiyarsa ga wadannan kungiyoyin da sauran magoya bayan wannan gwamnatin tare da tabbatar da masu da cewa jam'iyar Apc ba za ta taba yar da su ba 

Yusuf Idris Gusau 
Sakataren yada labarai na jam'iyar Apc na jihar Zamfara  
5th May, 2022

Post a Comment

0 Comments